Wednesday 4 June 2014

WASU DAGA CIKIN MAGANGANUN ASH-SHEIKH ALBANI ZARIA A LOKACIN RAYUWARSHI (PART 8)

Duk wandanda akace ya amshi sarauta wai shine sarkin musulmi na Nigeria! 

Duk wanda akace ya zama gomnan sokoto! 

Alama na farko in ance shi wai Ahlussunnah ne, toh yayi 'kokarin kawar da hubbaren Shehu ya bar 'kabarin Shehu yadda yake indai ya ce Shi Ahlussunah ne da gaske. 

Hubbaren Shehu ta sabama karantar Shehu. Sarki da Gomna ku tara Malamai kuce a kawo dalilai,a bude littattafan Shehu a ji yadda 'danfodio ke kafirta masu yi mishi abubuwan da ake mishi a 'kabari.

(VIA: KARATUN LITTAFIN SHARHUS-SUNNAH KASET NA TARA)

No comments:

Post a Comment